Chapter 135
Chapter 135
jira, dama in ace ma zan ƙara waiwayar gidan Hayyo to ace Auta na hannunsa ne, yanzu kuwa da bata wurinsa banga dalilin da zaisa in taka ƙafata a ƙofar gidansa saboda ina da wata ajiyar a gidansa ba, Hamid namiji ne baya buƙatata kamar yanda Auta ke buƙatata". Kaka tace,"bafa zance ake na ki dawo da shi hannunki ba, kije ya ganki yasan kina raye kuma kina cikin ƙoshin lafiya shine maganar da nake yi miki". Ummi tace,"ba yanzu ba Dada". Kaka ta gyaɗa kai tace,"ai shikenan ban san lissafin da kike yi ba. ni Allah yasa ma ta hanyar arziƙi Hayyo yayi kuɗin da aka ce yayi". Ummi tace,"ni banma yarda da yaron da ya faɗa ba". Fillo tace,"Ummi da gaske ne fa, ai sanda ku ka tafi gidan Inna Azimi munje ni da su Badariyya, da muka shiga matan gidan suka ce ai kusan wata huɗu kenan da suka sayi gidan, masu gidan sunyi kuɗi sun tashi, to ni naso ma na tambayi inda suka koma kawai na fasa". Ummi dai bata ce komai ba tayi shiru, ita ai banda ma dai bata son musawa maganar mahaifiyarta ai bata ga me zai sa su ƙara komawa Taraba ba a rayuwarsu, tunda Allah baisa sunyi dacen dangi ba, ita bata yi dacen miji ba, ƴan'uwan Kaka kaf ba wani kula suke da ita ba, kamar ma ba ciki ɗaya suka fito ba ayanda suke nuna mata, kansu da matansu kawai suka sani, dalilin da ya dawo da Kaka nan gombe kenan ta samarwa kanta mafita na neman aiki a gidan sarki, daga nan kuma ta koma gidan Dikko ga kuma matsayin da Allah ya kawo su ayau. Maijidda ta shigo parlon bakinta ɗauke da sallama, su Kaka suka amsa mata ta nemi wuri ta zauna tana kallon Fillo dake jikin Ummi tana hararta da cewa,"Ummi dan Allah ki daina ɗora wannan ƙatuwar abar a jikinki". Ummi na murmushi tace,"autar guda?". Maijidda ta taso ta taho tazo itama ta ɗora kanta a kafaɗar Ummi tana cewa,"Ummi to nima ai autar ce". Fillo tasa hannu ta tureta tana faɗin,"dilla ɗaga min uwa, da wani ƙaton kanki anan zaki ce zaki kwanta jikinta salon kija kafaɗarta tayi ciwo". Maijidda ta harareta tana mayar da kanta wurin Kaka tace,"Kaka Yami tana gaisheki, wai ki bada wannan saƙon da za'a kawai Baba Huraira zata je gidan gobe". Kaka tace,"aiko gwara da Allah yasa ta tuna min, jeki ɗakina ɗauko wannan baƙar jakar tawa ta gado ki kawo min". Maijidda ta shiga ta ɗauko jakar ta dawo, Kaka ta ɗauko saƙon ta bata tana yi mata bayani. sannan ta ɗora da ce mata,"yauwa kuma ki faɗa mata jiya fa an karɓo kuɗaɗenmu na wajen matsiyacin yaron can, an karɓo miliyan shidan duka wallahi". Maijidda tace,"shege ai ni naso jefe ɗan iska akayi kowa ya huta da annoba". sai kuma cikin tsokana tace,"umm in iya bakina kar Fillo ta ƙullace ni". Fillo ta miƙe a jikin Ummi tana hararta tace,"banza kawai". ta faɗa tana tashi ta wuce ɗaki. Ummi tace da Maijidda,"kin fara zuwa yiwa su Hajiya Madina aikin?". tace,"ehh Ummi tun washe garin ma da ku ka taho ai". Kaka tace,"to Maijidda sai ki kula da Allah, na san ki kema hankali da natsuwa ba daga nan ba, dan haka ki iya zamanki da mutanen nan, ki zama me gaskiya da amana da kula da aikinki, kina ganin dai ta dalilin iya zama da su da Fillo tayi alkhairin da suka yi mana, bacin haka wa zai ɗauki gida sukutun guda ya bamu kyauta?, waye zai tsaya tsayin daka akan a karɓar mana hakkinmu wajen wancan azzalumin bawan?, aini babu abinda zance da Hajiya Madina sai dai ubangiji yayi mata sakayya da gidan aljannah, mutuncin matar nan ya wuce duk mutum yake zato wallahi". ƙarar wayar Kaka ta katse maganartata, ta ɗaga tasa a kunne ba tare da ta san waye me kiran ba dan bata iya karanta sunan ba. sai bayan kuma ta ɗaga ɗin ta ɗau muryar Dr Yusuf daga can ɓangarensa da yay sallama, bayan gama gaisawa ta tambayesa iyalin da mutanen gidan sannan yace ta bawa Ummi. Ummi na murmushi ta amsa sallamarsa tace,"Shikenan kuma sai ɗana ya manta da ni". Dr Yusuf ya sosa ƙeyarsa yace,"na isa na manta dake Mommi, wallahi kullum sai munyi kewarki, Mommi ban san me yasa kika ƙi yarda kici gaba da zama a wurinmu ba, ko mun miki laifi ne Mommi?". Ummi tace,"kul Yusuf naji ka ƙara ambatar kun min laifi, ni dai kawai abinda nake so ku sani shine har duniya ta naɗe ba zan manta daku ba da alkhairin da ku kai min, ina nan zan ƙara zuwa na musamman in ƙara godiya, ina jikata Farha?". Dr Yusuf yace,"tana lafiya Mommi, jiya ma Nuratu ke cewa tana so tazo ta gaida ke, to kuma sai naji kamar Maijidda tace kun bar can gidan Alƙali". Ummi tace,"ehh wallahi, ai sun sallami Kaka daga aikin da sha tara ta arziƙi, sunce taje ta huta haka, wallah kam sun bamu gida anan Dubai Quaters, baka gida ba Yusuf so masha'Allah, dama nace sai munyi waya tukunna sai in sanar muku insha'Allahu, to ashe ma Maijidda ta rigani". yace,"masha'Allahu, Allah ya saka musu da alkhairi". "ameen Yusuf, dan Allah ka gaidar min da su Nuratu da Ammi da Umma, kai da kowa ma musamman Inna Wuro, gaisuwarta tafi ta kowa yawa". yace,"insha'Allah Ummi duk zasu ji, sai munzo gaisuwa". "to Allah ya kawo ku, ina nan ina zuba ido". daga haka suka yi sallama, Maijidda na murmushi tayi tafi tace,"mu dai abinmu sharr". ta faɗa tana kallon Fillo data fito cikin complete shirinta na tafiya makaranta, ta gimtse dariyarta Fillo ƙuma ta galla mata harara tana cewa da Ummi,"na fito Ummi". ta zauna Ummi ta dafa kanta tayi mata adu'a sosai, tana ƙara ce mata ta kula. Kaka da zolaya itama tace,"ke kuma sai da angon naki ya kashe wayar sannan za ki fito, wannan kiran dai ai nasan ba namu bane, naki ne ake wani wayance da Ummi ake nema". Fillo ta turo baki tace,"angon wata dai amma bani ba, me zanyi da wannan". ta faɗa da duk gaskiyarta. Ummi ta waro ido waje tace,"iye! Auta ɗan nawa kike cewa me zaki yi da shi?, ban da shi Auta kin isa yanzu ki ƙara saka ni a idonki?, ah lallai, wato babu ko kunya a gabana kike faɗin me zaki da ɗana, ba ki san nafi sonsa ba akanki". cike da shagwaɓa kamar zata yi kuka tace,"Ummi ni to ba zan auri me mata ba, dan Allah ku daina haɗa ni da shi". Ummi na ƴar dariya tace,"idan kin kwantar da hankalinki ma nima ba zan yarda ayiwa ƴata Nuratu kishiya ba, ah tou can ki yanka kije ki samo daidai dake ɗin, nima ɗana yafi ƙarfinki dan ba abinda zai yi da ƙwaila irinki". ta miƙe cike kunya tana barin kusa da Ummi tace,"ni bama yanzu ba ai, sai na zama barrister tukunna in zaɓa in dirje, by then Abba nah ya shiryu ya gane gaskiya sai yazo ya ɗaukemu, mu koma can inda muka fito sai mu bar tsohon ɗan naki anan da shi da gwalagwajin matar tasa". ta faɗa tana ƴar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188
- 189 Chapter 189
- 190 Chapter 190
- 191 Chapter 191
- 192 Chapter 192
- 193 Chapter 193
- 194 Chapter 194
- 195 Chapter 195
- 196 Chapter 196
- 197 Chapter 197
- 198 Chapter 198
- 199 Chapter 199
- 200 Chapter 200
- 201 Chapter 201
- 202 Chapter 202
- 203 Chapter 203
- 204 Chapter 204
- 205 Chapter 205
- 206 Chapter 206
- 207 Chapter 207
- 208 Chapter 208
- 209 Chapter 209
- 210 Chapter 210
- 211 Chapter 211
- 212 Chapter 212
- 213 Chapter 213
- 214 Chapter 214
- 215 Chapter 215
- 216 Chapter 216
- 217 Chapter 217
- 218 Chapter 218
- 219 Chapter 219
- 220 Chapter 220
- 221 Chapter 221
- 222 Chapter 222
- 223 Chapter 223
- 224 Chapter 224
- 225 Chapter 225
- 226 Chapter 226
- 227 Chapter 227
- 228 Chapter 228
- 229 Chapter 229
- 230 Chapter 230
- 231 Chapter 231
- 232 Chapter 232
- 233 Chapter 233
- 234 Chapter 234
- 235 Chapter 235
- 236 Chapter 236
- 237 Chapter 237
- 238 Chapter 238
- 239 Chapter 239
- 240 Chapter 240
- 241 Chapter 241
- 242 Chapter 242
- 243 Chapter 243