Chapter 4
Chapter 4
da har zancen aure ya shiga? And beside wannan mutumin shine ya kwashe mana kamfanin mu da abubuwa da dama namu ,kuma yake cigaba da mun barazana a rayuwa..." "Momy nooooo! Komai zai zo qarshe komai namu zasu dawo,kamfaninmu gidanmu mutuncin mu... "Ki mun shiru yusra kar in kodeki da mari ,duk abinda kika lissafa bana muradinsu ,Ni ke nike so kiyi farin ciki basu ba don haka bazan baki wanda zai hana maki farin ciki ba" "Momy na sanshi mutumin kirki ne kuma kema kina fada ,kar takan dan qaramin saɓanin nan ya shiga ki manta alkhairinsa momy" "Yusrah ke Yarinya ce 🤧 Mutum ba abun yarda bane kuma kowani lokaci yana iya sauyawa..." "Momy ina mahaukacin sonsa kuma wallahi wallahi indai ba'a bani shi ba ko insha poison in mutu ko in gudu in ɓata baza ku qara ganina ba a duniya.....period" Ta miqe ta fice fuuuuu,tabar Hajiya Juwairiyya cikin tashin hankali da kasala Oum Aphnan [6/15, 8:17 AM] Chuchu👻: 10 days later "Why Are You intended to marry me ,i mean what is ur plan? Kuma tsawon yaushe zamu dauka muna auren kafin mu rabu kowa ya kama gabansa" "Sai sanda na shirya" "Humm zakuwa kai experiencing worse thing a wannan auren don ko abinci ban iya ba ma ,not like..." "Karki damu abincin ma bana ci da rana ai ,da daddare just a tea or coffeee" Shigowar Hajiya mama wato surukuwar Yusrah kenan step mom din Major Adeel yasa duk sukayi shiru . Da fara'arta ta samu kujera ta zauna bayan koran en gidan da suka zo gaishe su da akayi don a bata damar taci abinda aka kawo masu as a Guest kuma sabuwar surukuwar gidan inshaAllah. "Kyakkyawar diyata ,to ina gida ya Iyayen naki suna lafiya dai" "Lafiya lou mama" "To mashaAllah wlh munji dadin wannan abu kuma Allah yayi albarka ,Allah ya hade kanku ya kauda fitina ,halan kun dade ma tare?" Caɓe baki tayi gamida girgiza kai "kwana 10" Da sauri Major Adeel ya diddilo ido yana son kare maganar . "Haba Yusrah don matata ta mutu dont deny it ,Hajiya mama watan mu 8 tare fa " Sunkuyar da kai yusra tayi tana magana a hankali wanda shi kadai zai ji ta "Ƙaryaaa" Girgiza kai yayi yana dariya ,itama Hajiya mama haka nan taji sun bata sha'awa yarinyar kanta akwai wauta da quruciya. "Mohammed ga dukkan alamu munyi sa'ar surukuwa a karo na biyu ,amma ko zaka iya fada mun me yafi burgeka da ita? Kasan in zakuyi aure kasan me yasa ma kake so ka auri partner dinka ,kasan me take so da meye bata so not like i love You na shirme ba Pov" Kallon qasa qasa Yusrah take masa lallai yau an qure sa ! She exclaimed. "Wallahi abu na farko da ya burge Ni da ita shine smartness dinta.." da sauri Yusrah ta bashi amsa da "Gadara ne!😎" Kautar da fuska yayi kamar baisan tana yi ba"sannan ita din ta daban ce ko a cikin mata" "Izza ne🤨" "Sannan er gayu ce mama" "Self courage ne🫤" Hajiya mama rafka tagumi tayi tana kallonsu kamar wasu masu shirin wasan kwaikwayo. Itakuma sai jujjuya ido yusran takeyi tana magana a nutse ba shayin kasancewarsa soja ko wani abu ko kuma fa tayi tunanin a gidan surukanta take . "Me yasa kuke son ku auri junanku da wirwuri haka Adeel matanka ko arba'in bata yi ba..." Kafin ya bata amsa Yusrah tai karaf tace "Personal purpose ne mama ,wani dalilin mune kawai mama" Yarinyar fa kanta na hayaqi,matsalar yaran Abuja din nan kenan ɗiyoyin masu kuɗi akwai gadara ! Amma Instead taji yarinyar batayi mata ba sai ji tayi kamar tana qara burgeta. "Amma ɗiyata ...." Kafin maman tayi magana tayi gaggawar dafe kai "Kash mama wlh wlh Ni mutum ne marasan yawan tambaya ,duk na zama exhusted ki yi hakuri in na shigo family din naku kya yimun duk tambayoyin da kuke so ...(ta juya ta kalli Adeel) bakace mun gidan ku in ana so a aure ku Ku maza ana dinga titsiye mutum da tambayoyi ba kamar gidan mahukunta ko Alkalai ....anyways plz ina mota in ka gama kazo ka maidani gida" Ta mike batajira cewan kowa ba tayi wucewarta. Oum Aphnan [6/15, 7:15 PM] Chuchu👻: A month later Duk yanda momy Juwairiyya taso ta hana auren amma Yusrah she insisted,don haka ta sanar ma dangin mahaifin Yusrah ,maganar auren ƴarsu ,sunji dadi sosai saboda a zamanin nan da ya lalace in yaro ya samu inda zai zauna yayi zaman aure to ba abunda ya fishi dadi ,bare kuma ita marainiya da mahaifinta ya rasu suna can suna nan basu san ya yanayin tarbiyyar ta yake ba a wajen mace ,duk da dai sun san Hajiya Juwairiyya mace ce mai addini kuma tsayayya amma kuma duk da haka suna sane sarai Yusrah taɓararriyar yarinyace Shiyasa sunsha mamaki ma da ta yarda ayi mata aure da wuri........Ni kuwa nace rashin sani. Tuni dangin Adeel suka hallara a babbar gidan su Yusrah kuma a yanda sukaje tambayar neman izini da saka rana ,bayan sun gabatar da komai Adeel ya roki a daura masu aure nan take tunda dai amaryar ta yarda da haka kuma sun fahimci juna kuma dai akwai dama na iya yin duk wani hidima da ya dace to babu bukatar sai an jata da tsayi tunda duk waliyyan Ango da amarya sun hallara. Aure da mutuwa isuwar ubangijine Allah ke sa ayi shi a sanda yaso don haka ,babu ɓata lokaci aka daura aure dangi na nesa suka biyo jirgi saidai Hajiya Juwairiyya Sadiq ta ji hayaniyar dangi daganan aka shiga shagalin biki aka saka Yusrah a lalle washekari akayi kamu . Tun kafin a watse wajen kamu dangin ango suke shelan duk wanda zaije ganin gidan amarya to ga motoci nan don babu wanda zai kwana ,amarya kuma ango da kansa zai zo ya dauki abarsa🫤love nwantiti. Tunda dangin amarya sukaji haka sukayi ta ɓururuwar zuwa ganin gidan amarya ,gidan sane dai inda matarsa ta rasu a ciki amma an sauya masa fasali dingurgum kudi kenan masu gidan rana . Sai qarfe tara da rabi na dare Adeel ya taho cikin farar ferrari daukan amarya .Yusrah kam ido qemandagas don ita duk bidirin da ake bata dauke shi aure ba tasan dai auren manufa ne ,to meye nata na tayar da hankali ? Kwana nawa ne zata dawo gidansu ta nema zuqeqen miji ta aura? En uwa da dangi suka shiryo Yusra cikin gown me mugun tsada suka lullube mata kai suna sakata a mota . Sai a sannan ne Major Adeel ya dinga hotuna da danginta don tunda aka daura auren ba wanda ya sake ganin qeyar ango ,itama kuma dama amaryan ba qawaye ne da ita ba don haka a sauka lafiya hutaroro . Sai sha daya saura kwata suka fice daga gidan ana ta masu addu'ar zaman aure me cike da zaman lafiya mai daurewa suka rankaya zuwa gidansu . Ita dai Yusrah ba uhm ba uhm uhm kanta na sunkuye tana chatting da wayarta abunta har suka iso gidan .sai da sojoji suka bude masu gate guda uku kafin suka isa asalin harabar gidan. Lallai komai ya sauya ji gida? Ni sanda
Table of Contents